Dattijon Arewa Ya Yi Kira Ga Hukumomi Kan Lamarin El-Rufai
Ibrahim sahabi
Ya ce idan har ana zarginsa da wani laifi, ya kamata hukumomi su fito su bayyana hujjojin da ke tabbatar da zargin a fili.
A cewarsa, a kasa mai bin dimokuradiyya ba daidai ba ne a rike mutum ba tare da bayyana laifin da ake tuhumarsa da shi ba.
Ya kara da cewa ko mutum yana goyon bayan siyasar El-Rufai ko baya goyon bayanta, dole ne a tabbatar an bi doka.
Dr. Baba-Ahmed ya bayyana haka ne a wani sako da ya wallafa a shafinsa na Facebook, inda ya jaddada muhimmancin adalci da gaskiya.
Comments
Post a Comment