“ADC Ta Samu Sabbin Shugabanni: Aliyu Lawal Ibrahim Ya Yi Alkawarin Cikakken Goyon Baya Domin Nasarar Jam’iyya”
jigo a jam’iyyar ADC, Alhaji Aliyu Lawal Ibrahim Cairo, ya bayyana godiyarsa ga Allah Madaukakin Sarki bisa kammala zabukan cikin gida na jam’iyyar daga matakin gunduma, karamar hukuma da kuma jiha cikin lumana da nasara.
A cikin wata sanarwa da ya fitar a yau Lahadi, Aliyu Lawal Ibrahim ya taya sababbin shugabannin jam’iyyar murna, inda ya bayyana cewa ADC jam’iyya ce mai albarka wadda ke da kyakkyawar makoma idan aka hada kai aka yi aiki tukuru domin cimma buri.
Ya kuma tabbatar da cikakken goyon bayansa ga sabbin shugabannin, yana mai cewa a shirye yake ya bayar da gudunmawar da zai iya domin saukaka ayyukansu da kuma tabbatar da nasarar jam’iyyar a zabubbuka masu zuwa daga sama har kasa.
Haka zalika, ya bukaci shugabannin da ‘yan jam’iyya da su yi amfani da damar da ke gabansu wajen hada kai da kuma bude kofa ga duk masu niyyar tallafawa jam’iyyar domin ganin ta samu rinjaye a dukkanin matakan zabe.
A karshe, ya yi addu’ar Allah ya taimaki shugabanni da al’umma, tare da fatan alheri ga Malam Ahmad Nasiru El-Rufai, jihar Kaduna, garin Zariya da kuma kasa baki daya, yana mai cewa Allah ya albarkaci jam’iyyar ADC.
Comments
Post a Comment